Rashin Lafiya Mai Tsanani Ta Kama Jaruma Jamila Nagudu

Yanzu haka labarin da ke zuwa mana na nuni da cewa fitacciyar jarumar nan ta masana’antar Kannywood Jamila Nagudu na kwance a asibiti.
Jarumar wadda cikakken sunan ta shine Jamila Umar an ce tana kwance a wata asibitin kudi ne dake a birnin Kaduna dake a arewacin kasar nan inda take jinyar ciwon da ke damun ta.
Amanagurus ta samu labarin cewa fitacciyar jarumar dai ce ta saka hoton nata a bisa kafar sada zumuntar nan na Instagram tana a kwance a gadon asibiti.
Ya zuwa yanzu kuma rahotannin da muka tattaro sun nuna mana cewa jarumar tana fama ne da citar nan ta tsakuwar ciki watau Appendix a turance kuma har ma an yi mata aiki a asibin.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Rashin Lafiya Mai Tsanani Ta Kama Jaruma Jamila Nagudu"

Post a Comment