Za a fuskanci wahalar man fetur a Nigeria — NUPENG

A ranar Litinin ce direbobin manyan motocin dakon man fetur za su fara yajin aiki a Najeriya.
Kungiyar kwadago ta ma'aikatan dakon man fetur da iskar gas NUPENG, ta ce za tu shiga yajin aikin ne saboda karancin albashi da lalatattun titunan kasar da suke bata musu motoci.
Wani mai magana da yawun kungiyar Cogent Ojobo, ya yi gargadin cewa za a fuskanci wahalar karancin man fetur da dizal da kananzir a kasar, saboda za su dakatar da rarraba su.
Ya kuma ce ba a saka ranar da ake zaton daina yajin aikin ba.
Hakan na nufin tattaunawar da aka yi tsakanin NUPENG da gwamnatin tarayyar Najeriya bai yi tasirin hana kungiyar shiga yajin aikin ba.
Ma'aikatan NNPC sun fara yajin aiki
Nigeria: Litar man fetur ta koma N145
Ma'aikatan mai sun soma yajin-aiki a Nigeria
Wannan ba shi ne karo na farko da kungiyoyin kwadagon ma'aikatan man fetur ke shiga yajin aiki ba a Najeriya, kuma a duk lokacin da suka shiga to ana fuskantar matukar wahalar man a kasar.
Tun a ranar Asabar hankalin 'yan kasar ya fara tashi sakamakon rade-radin yajin aikin da suka ji, inda gidajen mai suka fara cika da motoci.
Mutane sun ta cika tankunan motocinsu da mai, har ma suna saye a jarkoki duk saboda tanadi don tsoron fuskantar wahalar karancin man.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Za a fuskanci wahalar man fetur a Nigeria — NUPENG"

Post a Comment