Zaben Kaduna: Kona ci ko na fadi a soke zabennan kawai>>Sanata Shehu Sani

Sanata Shehu Sani me wakiltar Kaduna ta tsakiya a majalisar Dajjitai kuma dan takarar Sanata na jam'iyyar (PRP)ya bukaci da a soke zaben jihar Kaduna, musamman na mazabarshi, Kaduna ta tsakiya saboda matsalolin zaben sun yi yawa.
Sanatan ya bayyana hakane ga manema labarai kamar yanda jaridar The Nation ta ruwaito, ya ce ya aikawa hukumar zabe hujjojinshi akan cewa a soke zaben, yace duk da cewa basu samu sakamakon zaben daga hukumar zabe ba amma koma yaya sakamakon zai kasance sudai bukatarsu shine a sokeshi.

Sanatan yace an yi amfani da jami'an tsaro wajan yin magudi da kuma yiwa masu zabe ba daisai ba.

Source: hutudole

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Zaben Kaduna: Kona ci ko na fadi a soke zabennan kawai>>Sanata Shehu Sani"

Post a Comment