Ndume ya sake cin zaben Sanata daga Borno

Tsohon shugaban masu rinjaye na majalisar dattawan Najeriya, Sanata Mohammed Ali Ndume, na jam'iyyar APC ya sake yin nasara a zaben majalisar dattawa inda ya samu kuri'a 300, 637 yayin da abokin hamayyarsa na PDP, Kudla Haske, ya samu kuri'a 84, 608, kamar yadda baturen zaben yankin Farfesa Isa Hassan ya bayyana.
Wannan shi ne karo na uku da Sanata Ndume zai wakilci Kudancin Borno a majalisar dattawan Najeriya.

BBChausa.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Ndume ya sake cin zaben Sanata daga Borno"

Post a Comment