Donald Trump ya sake musanta kutsen da aka zargi Rasha da yi a Zabe

Shugaban Amurka mai jiran gado Donald Trump
ya sake nuna shakku a kan zargin da ake na
cewa Rasha ta yi katsalandan a zaben Amurka
da aka yi a shekarar da ta gabata.
Ka Mr Trump ya yi a shafin Twitter sun zo ne
sa'oi kafin jami'an leken asirin Amurka su yi
masa karin haske kan dalilin da ya sa su ka yi
imanin cewa Rasha ta umarci masu kutse a
shafin intanet da su yi wa abokiyar hamayyarsa
ta jam'iyyar democrats Hillary Clinton zagon kasa
a lokacin zaben.
A martanin da ya mayar, mataimakin shugaban
kasar Joe Biden ya ce matukar rashin hankali ne
ga Trump ya ce yana shakku kan wani abu da
jami'an hukumar leken asirin kasar suka fada.
Tuni dai shugana Obama ya karbi rahoton
hukumomin wanda ya ce manyan jami'an
gwamnatin Rasha sun cashe da suka samu
labarin cewa Trump ya samu nasara a zaben.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Donald Trump ya sake musanta kutsen da aka zargi Rasha da yi a Zabe"

Post a Comment