Labarai Cikin Hotuna: Gwamna Ibrahim Shema A Yayin Daya Isa Kotu Don Amsa Tambayoyi

A dazu kenan da mai girma tsohon gwamnan jihar Katsina barrister Ibrahim Shehu Shema ya bayyana a gaban babbar kotun saurarar kararraki dake jahar katsina don amsa tambayoyi da hukumar yaki da rashawa ta EFCC zasu yi masa.
Shema wanda yake sanye cikin dinkin babbar riga na shadda mai ruwan kasa ya samu rakiyar chairman PDP na jahar katsina, tsohon chairman party Rabiu Gambo Bakori, sakatare, kwamishinoni da sauran magoya bayansa.
Daga cikin mahalarta taron kotun akwai SSG na jahar, Mustapha inuwa da kuma mai ba gwamna shawara akan harkoki na musamman wato Alhaji Tanimu Sada.
Duba hotunan a kasa...

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to " Labarai Cikin Hotuna: Gwamna Ibrahim Shema A Yayin Daya Isa Kotu Don Amsa Tambayoyi"

Post a Comment