Fargaba kan jinkirin sakamakon zabe a Ghana

Majalisar tabbatar da zaman lafiya ta Ghana ta
yi kira ga hukumar zaben kasar EC da ta
gaggauta sanar da sakamakon zaben shugaban
kasar da aka yi a ranar Laraba.
Shugaban Majalisar Farfesa Emmanual Asante
ne ya yi kiran a wajen wani taron manema
labarai.
Farfesa Asante ya ce jinkiri wajen bayyana
sakamakon ya na haifar da fargaba, da rashin
tabbas, da kuma yada jita-jita mara amfani.
Ya kuma yi kira ga jam'iyyun siyasa da jama'ar
kasar su kwantar da hankula, su kuma jira
hukumar zaben kasar ta bayyana sakamako.
A nata bangaren, hokum zaben kasar ta ce
jinkirin na da nasaba da matsalolin da aka samu
a wurin yin zaben fiye da kima.
Hukumar ta ce don haka sai ta sake tantanace
duka sakamakon da aka kawo mata, kafin ta kai
ga bayyana wa.
Ita kuwa gamayyar kungiyoyin fararen ta cikin
gida da ta saka ido kan zaben, CODEO, ta ce
zaben yana da inganci.
CODEO ta kuma yi Allah-wadai da yadda
jam'iyyun siyasa ke bayyana sakamakon zabe,
gabanin hukumar zabe.
A wani labarin, bayanai sun ce jakadan Amurka a
Ghana ya kai ziyara ga dan takarar jam'iyyar
hamayya Nana Akuffo Ado a gidansa da safiyar
ranar Alhamis.
Gidan talabijin na Joy News mai zaman kansa ya
rawaito cewa mutanen biyu sun gana a asirce,
kuma babu wanda ya san abin da suka tattauna.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Fargaba kan jinkirin sakamakon zabe a Ghana"

Post a Comment