Likita ya tara haqoran da ya cire wa marasa lafiya dubu 10 a Abu Dhabi

Wani Likita a birnin Abu Dhabi na Hadaddiyar
Daular Larabawa, mai suna Dokta Nizar
AbdurRahman ya tara hakoran marasa lafiya
dubu 10.
“Wasu marasa lafiya na adana hakoran da aka
cire musu saboda dalilai na addini,” a cewar
likitan, wanda ya shafe shekara 15 yana aiki a
Abu Dhabi.
“Na shafe shekara 13 ina aiki a Cibiyal kula da
Lafiya ta Baniyas Ahalia, sannan na yi shekara
biyu a asibitin Al Ain,” inji shi.
“Ina burin samun lambar yabon kundin tattara
shahararrun al’amura na Limca da ke kasar Inda,
da kuma na duniya, wato Guiness world Record,
bisa la’akari da abin da na tara.”
Ya tara daukacin hakoran da aka cire a asibitin,
inda yake tsoma su a ruwan sinadarin Hydrogen
Perodide.
“Nakan wanke su da maganin kariya daga
kwayoyin cuta.Kuma akwai hakoran manyan
mutane a cikin tarina,” a cewarsa.
“Kodayaushe nikan bai wa majinyata shawar su
ci gaba da kula da hakoransu, har ta kai ga in
babu yadda za a yi sai a cire,” inji Likita.
Yana taimaka wa dalibai wajen aikin gwaji.
“dalibai kan untube ni in suna bukatar hakora.
Don su yi amfani da su a jarabawar gwaji, ko
cike gurbin hakorin da ya fadi,” inji shi.
dabi’un masu ciwon hakori da na gano Likita
Nizar a fahimci dabi’un masu fama da ciwo daga
sassan duniya daban-daban a tsawon shekara 15
da ya shafe yana aiki.
“Mutanen da suka fito daga Indiya, musamman
na birnin Kerala ba su cika zuwa asibiti ba, har
sai ciwo ya matsa musu. Sukan yi amfani da duk
maganingida da zai taimaka musu, sai lamarin ya
ci tura sannan su je asibiti. Mutane bas u fahimci
cewa zuwa asibiti da wuri zai ceci hakoransu.
Domin ba a zaune nike don cire musu hakori
kawai ba,” inji shi.
“su kuwa al’ummar Pakistan, musamman
wadanda ke makale da biro a aljihu, za su yi
kokarin bayyana maka yadda suke so a yi musu
aiki. Ba za ma su saurareka ba. Idan ka biye
musu, kana iya cire hakorin da ba shi ne mai
ciwon ba, inda a karshe sai an dawo an yi abin
da ya dace,” acewarsa.
Su kuwa mutane Bangladash, y ace, masu
tababa ne. “Kimanin kasha 90 cikin 100 na
wadannan mutanen suna tunanin idan an cire
musu hakori za su rasa ido. Don haka nike yi
musu alkawarin idona, ta haka nike jan ra’ayinsu
su amince a yi musu aiki.
Mutanen Afirka kuwa hakoransu na da kwari.
Nizar ya ce gogewarsa ta kai ga zai iya bayyana
maka sana’ar mutum idan ya dubi hakoran
marasa lafiya. “Zan iya tantance tela da mai
aikin lantarki. Suna da ramuka hadaddu a
hakoransu,”
“Na sha ganin marasa lafiyar da suka shafe
shekara 15 zuwa 20 ba su goge bakinsi ba,
amma suna son fara’arsu ta fito da hakora masu
haske kamar jaruman Hollywood. Irin wadannan
matsalolin suna da wuyar sha’ani.”
Abinci na da tasirin inganta kwarin hakori, don
haka sai a rika taunawa da kyau, kamara yadda
likitan hakori kan bayar da dabarun inganta
hakori. Ruiwan lemu mai dauke da iskar gas na
matukar cutar da hakora. Hatta shayi da gahawa
na cutar da su.
“Yawan tauna abinci na kara karfin hakori,” inji
shi.
A cewar Dokta Nizar samun managartan hakoran
ba abu ne mai wahala ba. Shawarar da ya fi bai
wa mutane wajen goge hakori, ita ce: “A goge
baki da buroshi mai laushi kuma a hankali. Domin
goge hakori ba kokowa ba ce.”
“akwai bukatar mutum ya goge hakorinsa sau
biyu a rana, kuma ya kuskure da sinadarin kariya
daga cuta. Sannan, mutum ya rika zuwa ana
duba hakoransa bayan wata shida. Kuma rika
zuwa gurje hakora a asibiti.
Matar wannan likita, mai suna Simi Nizara, ita
ma likitar hakora ce, ta kuma fara tara hakoran
da ta cire daga bakin marasa lafiya.
“Ba ni da tarin hakora masu yawa,” a cewar
wannan Ba’Indiya ’yar asalin Punalur da ta fito
daga gundumar Kollam, ta kuma shafe shekara
hudu tana aiki da asibitin Al Salama da ke
Baniyas, a birnin Abu Dhabi.
Wannan likita a kullum yana ganin marasa lafiya
10 zuwa 12, sannan yana cire hakora biyar zuwa
bakwai a kowace rana. “Na fara tara wadannan
hakora ne don bayar da tabbbaci, amma yanzu
abin ya zame mini sha’awa. Shekara biyu da
suka gabatar tarin hakoran da nike da shi ba su
wuce dubu takwas ba. Yanzu kuwa tabbbas sun
wuce dubu 10.
Mai rike da kambin tarin hakora a likitocin Indiya,
shi ne Dokta Jibreel Oysul, wanda ya fito daga
yankin Tamil Nadu a kasar Indiya, inda a Kundin
shahararrun abubuwa na Limca, aka tabbatar da
cewa ya tara hakoran majinyata dubu 10, tun a
shekarar 2011.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Likita ya tara haqoran da ya cire wa marasa lafiya dubu 10 a Abu Dhabi"

Post a Comment