Ivory Coast: Za a gudanar da kuri'ar raba gardama kan kundun tsarin mulki

Ivory Coast zata gudanar da kuri'ar raba
gardama a yau akan sabon kundun tsarin mulkin
kasar wanda shugaba Alassane Ouattara ya ce
zai taimakawa kasar wajen samun cigaba bayan
shekarun da aka shafe ana fama da rikici.
Tuni dai jam'iyyun adawar kasar suka yi kiran da
a kauracewa wannan yunkuri, suna masu cewa
anyi saurin yiwa kundun tsarin mulkin gyare-
gyare kuma zai bawa shugaban kasar karfin ikon
da ya wuce kima.
Wani babban abu a cikin gyare-gyaren da ake
son yi a cikin kundun tsarin mulkin shi ne
saukaka ka'idojin zama dan kasa ga 'yan takarar
shugaban kasa, wani batu da ya rura wutar yakin
basasa har sau biyu a kasar tun shekarar 2002.
Sannnan kuma zai samar da majalisar dattawa a
kasar wadda kaso uku na adadinsu shugaban
kasa ne zai nada su.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Ivory Coast: Za a gudanar da kuri'ar raba gardama kan kundun tsarin mulki"

Post a Comment