Na fi so Ronaldo ya lashe Ballon d'Or — Zidane



Kocin Real Madrid Zinedine Zidane ya ce
Cristiano Ronaldo ne ya fi cancanta ya zama
zakaran kwallom kafar duniya duk da cewa bai
zura kwallaye da yawa a bana ba.
Zidane ya kara da cewa Ronaldo yana gaban
Lionel Messi wajen dacewa da lashe gasar ta
Ballon d'Or.
Ronaldo, mai shekara 31, na cikin 'yan wasan da
aka sanya sunayensu domin fafatawa wajen
lashe gasar bayan ya jagoranci Portugal ta dauki
kofin Euro 2016.
Sai dai ya yi ta samun koma-baya a kakar wasa
ta bana, inda ya zura kwallaye hudu kacal a
wasanni tara da ya buga.
Kocin na Real Madrid, Zidane, ya ce Ronaldo ne
"mutumin da ya fi dacewa da lashe gasar ba wai
don rawar da ya taka shi kadai ba, sai domin
tallafa takwarorinsa da yake yi domin su zura
kwallo."
Zidane ya ce Ronaldo ya san cewa nasarar da
yake tamu ta faru ne sakamakon aiki tukuru da
yake yi da kuma taimakwa 'yan wasan da ke tare
da shi.
Ronaldo, wanda sau uku yana lashe Ballon d'Or,
da kuma mai rike da kambun gasar Messi na
cikin 'yan wasa 30 da aka ware sunayensu domin
lashe gasar ta bana.
Dan wasan ya zura kwallaye 368 a fafatawa 357
da ya yi tun lokacin da ya koma Real Madrid
daga Manchester United a shekarar 2009.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Na fi so Ronaldo ya lashe Ballon d'Or — Zidane"

Post a Comment