Dan kasar Sin ya tuka keke zuwa aikin hajji a kasar Saudiyya

Wani Musulmin kasar Sin ya tuko keke zuwa
kasar Saudiyya don yin aikin hajjin bana, inda ya
samu kyakkyawar tarba a birnin Taif da ke
Yammacin kasar. kungiyar ’yan tseren keke sun
yi marhabin da wannan bawan Allah.
Mahayin keken ya ce ya taso daga gidanshi da
ke birnin dianjiang da ke Arewa maso Yammacin
kasar Sin, inda ya shafe tafiyar kilomita dubu
takwas da 150 kagfin isowarsa Yammacin
Saudiyya a birnin Taif.
Bayan da ya huta a wannan birni, sai ’yan
kungiyar tseren kekuna suka yi wa bakonsu
Muhammad dan Sin rakiya zuwa birnin Makkah,
kamar yadda shafin sadarwa na Sabk.com ya
ruwaito.
“Mu ne kungiyar tseren kekenuna a Saudiyya da
muka fara tarbar mahayin keke dan kasar Sin,
muna kuma fatan ganin ya samu irin wannan
tarbar daga kungiyoyi irin namu, don haka muke
gabatar da shi a sauran birane,” a cewar Nayef
Al Rawas shugaban kungiyar tseren kekuna ta
Taif.
A ranar Asabart din makon jiya ne Hukumar Kula
da Harkokin Addini ta kasar Sin (SARA) ta ce,
kimanin mutum dubu 15 da 500 ne Musulmin Sin
da za su yi aikin hajjin bana. Kuma tuna Juma’ar
makon jiya aka tura jira 37 su dauki alhazan Sin
dubu 11, wadanda suka tuni suka isa birnin
Makka a kasar Saudiyya, kamar yadda Kamfanin
Dillancin Labarai na dinhua.
Wannan lamari na tukin keke zuwa birnin Makkah
mutanen nahiyar Asiya sun saba da shi, don yi
hajji ko umra.
A watan Mayun shekarar 2014 wani gungun
mutanen Malesiya sun taso daga birnin Kuala
Lumpur zuwa birnin Madina. Mutanen su 12, sun
hawo kekuna takwas da wata karamar mota biye
da su, inda suka keta birane 53.
Mutanen sun shafe kwana 60 suna tafiya, don yin
umrah a birnin Makkah, kamara yadda jagoransu
ya bayyana.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Dan kasar Sin ya tuka keke zuwa aikin hajji a kasar Saudiyya"

Post a Comment