Manoma sun samu garabasar Naira miliyan 34 saboda dashen itatuwa a Sin

Manoman karkara a kasar Sin sun samu
garabasar Yuan miliyan biyar da dubu 600,
kimanin Dala dubu 850, wato daidai da Naira
miliyan 34, saboda kokarinsu wajen dashen
itatuwa a kauyen Lintao da ke Arewa maso
Yammacin kasar Sin a Lardin Ganasu, kamar
yadda kafar yada labarai ta Chinnanews.com ta
ruwaito.
Manoman karkarar da suka samu garabasar kudi,
yawansu ya kai magidanta 80 Zhang Zinhai, wani
da ya samu kaso mafi tsoka na Yuan dubu 100.
Ya ci burin dasa dimbin itatuwa a shirin dashen
badi.
Ya samu hanyar samun kudi mafi sauki fiye da
sauran al’umma, saboda a cewarsa: “Babu
bukatar kashe kudi a wannan aikin.”
A shekarar 2013, wani kamfani a kasar ya samar
da irin dashe na tsirran itatutuwa dubu 400 ga
daukacin magidantan da ke zaune a yankin.
Bayan shekara uku an yanke cewa manoman za
su mayar da yawan irin tsirran da aka ba su daga
kamfnain, inda aka tsara biyansu kudi. Shi kuma
kamfani zai sayar da wadannan bishiyoyi a
Artewacin kasar Sin, wato yankin Mongolia da
Shandi, ta yadda za su dasa korayen furanni a
yankunansu.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Manoma sun samu garabasar Naira miliyan 34 saboda dashen itatuwa a Sin"

Post a Comment