An kaddamar da littafi kan rayuwar Shugaban kasa Buhari a Abuja

A ranar Litinin da ta gabata ce aka kaddamar da
littafi a kan rayuwar Shugaban kasar
Muhammadu Buhari mai taken ‘Muhammadu
Buhari: The Challenges of Leadership in Nageria’
a zauren taro na Cibiyar ’Yar’aduwa da ke Abuja.
Tsohon Shugaban kasa, Yakubu Gowon ne ya
jagoranci bikin kaddamarwar, kuma ya bayyana
cewa Shugaba Muhammadu Buhari mayaki ne,
wanda ke aiki tukuru domin ganin ya farfado da
tattalin arzikin Najeriya, duk kuwa da irin manyan
kalubalen da kasar ke fuskanta.
Littafin, wanda shahararren malamin jami’a,
Farfesa John N. Paden ya rubuta, ya kunshi
bayanai ne a kan rayuwar Shugaba Buhari da
kuma gwagwarmayarsa tun daga shigarsa siyasa
zuwa yau. Marubucin, wanda shi ne ya rubuta
littafin tarihin marigayi Sardauna Ahmadu Bello,
ya bayyana Shugaba Muhammadu Buhari da
cewa mutum ne jajirtacce, mai kishin kasa,
wanda ke kokarin yin duk wani abu da zai
taimaki kasarsa. Ya kara da cewa, ya rubuta
littafin ne domin ya bayyana wa duniya ko wane
ne Shugaba Muhammadu Buhari.
Tsohon Shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya
yaba wa marubucin littafin, wanda ya ce ya
rubuta littafin da inganci. A cewarsa, duk wanda
ke son sanin Najeriya da shugabanninta, to ya
nemi littafin.
Shugabannin kasashen Chadi da Benin da Nijar
da ke makwabtaka da Najeriya sun halarci taron
kaddamar da littafin.
Sauran manyan mutanen da suka halarci
kaddamarwar sun hada da Mataimakin Shugaban
kasa, Yemi Osinbajo da Jagoran Jam’iyyar APC
na kasa, Asiwaju Bola Tinubu da Shugaban
Jam’iyyar APC na kasa, Cif Odigie Oyegun da
Alhaji Isma’ila Isa Funtuwa da Farfesa Ibrahim
Gambari da tsohon Jakadan Amurka a Najeriya,
John Campbel

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "An kaddamar da littafi kan rayuwar Shugaban kasa Buhari a Abuja"

Post a Comment