Kompany zai ci gaba da murza leda a City -Guardiola

Kocin Manchester City Pep Guardiola ya ce
Vincent Kompany na da kyakkyawar makoma a
kungiyar, amma yana bukatar sadaukawar domin
ya rika buga wasa akai-akai bayan raunin da ya
ji.
Kompany, wanda ya buga wa City wasa sau 22 a
kakar wasan da ta wuce, ya ce ya gaji a lokacin
wasan da suka yi da Manchester United ranar
Laraba, lamarin da ya sa aka maye gurbinsa da
Aleksandar Kolarov.
Guardiola ya ce, kwantaraginsa ba ta tare a
kungiyar ba don haka babu inda za shi, yana mai
cewa "Ya ji rauni sau da dama. Amma muna
kokarin sake ba shi damar buga wa."
Kompany ya dauki kofin Premier sau biyu a City
a shekarar 2012 da 2014, amma raunukan da ya
rika ji sun hana shi katabus a bana.
Ya buga wa City wasa 33 a shekarar 2014 zuwa
2015, kasa da wasa 37 gabanin hakan.
Kompany ya koma City ne daga Hamburg a
watan Agustan shekarar 2008 kuma
kwantaraginsa zai kare a shekarar 2019.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Kompany zai ci gaba da murza leda a City -Guardiola"

Post a Comment