Ana rikici kan limancin Masallacin Sultan Bello

Rundunar 'yansanda a jihar kaduna ta Najeriya ta
ce ta kama mutane 14 a yayin wata hatsaniya da
aka yi kan limacin masallaci mafi girma a jihar-
wato masallacin Sultan Bello.
Rikicin ya barke ne yayin sallar Jumu'a tsakanin
magoya bayan Sheikh Ahmad Mahmud Gumi da
na Dokta Khalid Aliyu wanda aka nada a
matsayin limamin masallacin na bayan tube
limamin na baya.
Magoya bayan Sheikh Ahmad Gumi na adawa da
nadin Dokta Khalid ne a zaman limamin
masallacin inda suke ganin gwanin nasu ne ya
kamata a nada.
Duka manyan malaman biyu dai sun dora alhakin
tashin hankalin kan junansu.
A wani taron manema labarai daya daga cikin
kungiyoyin musulmi mafi girma a kasar -
Jama'atul Nasril Islam ta yi Allah-wadai da
wannan lamari,inda ta yi kira ga gwamnati ta sa
baki kafin alamurra su kazance.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Ana rikici kan limancin Masallacin Sultan Bello"

Post a Comment