Kocin Jamus Low ya tsawaita yarjejeniyarsa

Kociyan tawagar kwallon kafa ta Jamus,
Joachim Low, ya tsawaita yarjejeniyar ci gaba
da jan ragamar kasar har zuwa karshen gasar
kofin nahiyar Turai ta 2020.
Kwantiragin Low, mai shekara 56, da Jamus za
ta kare ne, bayan kammala gasar cin kofin
duniya da za a yi a Rasha a 2018.
Low ya dade yana jan ragamar tawagar Jamus,
wanda ya yi wa Jurgen Klismann mataimaki na
shekara biyu, kafin ya karbi aikin horar da kasar.
Kociyan ya lashe kofin duniya da aka yi a Brazil a
shekarar 2014, a kuma shekara biyar ya kai
kasar wasannin daf da karshe.
A gasar cin kofin ahiyar Turai da aka yi a
shekarar 2016, mai masaukin baki Faransa ce ta
fitar da Jamus a wasan kusa da na karshe a
gasar.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Kocin Jamus Low ya tsawaita yarjejeniyarsa"

Post a Comment