Abin da ya sa ba zan taba Kwankwaso ba-Gwamna Ganduje

Gwamna Gaduje yace ba zai tsaya
binciken Gwamnatin Kwankwaso ba
– Gwamna Ganduje yace zai maida hankali
ne wajen yin ayyuka a jihar Kano
– Ganduje ne mataimakin Rabi’u
Kwankwaso lokacin yana gwamna
Gwamna Ganduje na jihar Kano yace ba zai
tsaya bata lokacin sa ba wajen binciken
gwamnatin Injiniya Rabi’u Kwankwaso.
Gwamna Ganduje ya bayyana haka ne a
Ranar Asabar dinnan, bayan taron Jam’iyyar
APC na bangaren Kano da aka yi a Garin
Sokoto.
Gwamna Ganduje yace duk da cewa mafi
yawan Jihohi suna ta binciken abin da ya
faru a Gwamnatocin baya, shi ba zai tsaya
yin wannan ba. Gwamna Ganduje ne dai
mataimakin Kwankwaso a lokacin yana
Gwamnan Jihar Kano har sau biyu; a
shekarar 1999-2003 da kuma 2011-2015.
Gwamna Ganduje yace abin da zai karkata
gare shi, shine ayyuka da tsare-tsaren da duk
za su kawo cigaba a Jihar Kano. Gwamna
Ganduje yace gwamnatin sa za tayi kokari
karasa duk ayyukan kwarai da ta gada daga
duk gwamnatocin baya wadanda za su kawo
cigaba ga Jihar Kano.
Ana ta rikici tsakanin magoya Kwankwaso da
shi Gwamna Ganduje, Gwamna Ganduje yayi
tir da abin da ke faruwa, yace wasu ne kawai
ke yada karya domin su ga bayan sa da
gwamnatin sa. Gwamna Ganduje yace
wannan abin Allah-wadai ne daga manyan
‘yan Kwankwasiyyan.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Abin da ya sa ba zan taba Kwankwaso ba-Gwamna Ganduje"

Post a Comment