Tsagerun Neja-Delta: Najeriya tayi asarar fiye da Tiriliyan 2

Kamfanin man Najeriya na NNPC tace
Najeriya ta tafka makudan asara daga
farkon shekarar nan zuwa yanzu
– NNPC tace Najeriya ta rasa akalla Biliyan
$7 watau fiye da Naira Tiriliyan 2 saboda
Tsagerun Neja-Delta
– Tsagerun Neja-Delta suna ta fasa butatan
man Kasar da yankin

NNPC GMD Baru
Kamfanin man Najeriya watau NNPC ta
bayyana cewa Kasar Najeriya tayi uban
asarar fiye da Naira Tiriliyan biyu daga
farkon shekarar nan zuwa yanzu. NNPC tace
daga Junairun shekarar nan, kawo yanzu
Kasar Najeriya ta rasa N2. NNPC tace daga
Junairun shekarar nan, kawo yanzu Kasar
Najeriya ta rasa Tiriliyan N2.1
Shugaban Kamfanin na NNPC, Maikanti Baru
yayi wannan bayani a Garin Abuja, wajen
gabatar da wata takarda game da farashin
man fetur da kuma tsageranci ‘yan yankin
Neja-Delta. Baru ya gabatar da wannan
takarda ne domin nuna alakar tsagerancin da
ake yi a Yankin da kuma abin da ake samu
daga man fetur din.
Najeriya ta rasa ganguna fiye da 7000
wannan shekarar, idan kowane ganga na kan
$45, Najeriya ta tafka asarar kusan Biliyan
$7 kenan watau fiye da Naira Tiriliyan biyu.
Kuma dai mafi yawan man da aka rasa na
gangar Gwamnatin Tarayya ne.
Shugaban APC Cif Oyegun yace an kauda
Boko Haram, kuma Gwamnatin Shugaba
Buhari na kokarin kawo karshen rikicin Neja-
Delta. John Oyegun yace Shugaba Buhari na
kokarin gyara, musamman ga abubuwa uku
kamar yadda ya dauki alkawari; tsaro, cin
hanci da kuma tattalin arziki.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Tsagerun Neja-Delta: Najeriya tayi asarar fiye da Tiriliyan 2"

Post a Comment