An dakatar da mata masu shirin talabijin a Masar saboda teva

Hukumomin talabijin a kasar Masar sun sallami
mata takwas masu gabatar da shirye-shirye
saboda teba, wai saboda manufar kafofin yada
labarai na kasar na kokarin kambama kimarta a
idon al’umma.
Wannan umarni dai an bayar da shi ne a makon
da ya gabata, inda aka bai wa matan wata guda
cur su yi kokarin rage teba kafin a kyale su su
dawo bakin aiki, kamara yadda kafofin yada
labaran kasar suka bayar da rahoto.
kungiyoyin fafutikar kare hakkin al’umma sun soki
lamirin korar mata takwas din, kuma mutane da
dama sun bijiro da tambaya kan cewa, ‘me ya sa
mata kawai aka kakaba wa dokar?’ Har yanzu dai
ba a tabbatar da cewa, ‘ko dokar za ta yi aiki a
kan mazan da ke gabatar da shirye-shirye a
gidajen talabijin ba, ko a’a.
Khadija Khatab, daya daga cikin mata masu
gabatar da shirye-shirye da aka sallama, ta yi tur
da wannan tsari. “Wannan kaskanci ne da abin
kunya,” kamara yadda ta bayyana wa jaridar Al
Watan.
“Wani yunkuri ne na korar masu gabatar da
shirye-shirye da suka goge da aiki, kuma a kyale
da za su ci gaba da aikin gabatarwar, alhalin ba
su da wasu managartan tsare-tsare,” a cewarta.
“kimanta nagartan aikin mutum bisa la’akari da
kiba ba ma’auni ne mai kyauta,” a cewar Eman
Beibers, shugabar kungiyar Bunkasa Harkokin
Mata ta birnin Alkahira. “Matsalarmu ita ce muna
auna kimar jiki a zahiri, maimakon aikin da
mutum ke yi. A gaskiya zan yi matukar
amincewa da dakatar da masu gabatarwar in da
a ce an yi la’akari ne da rashin ingancin aikinsu
ko suna caba kwalliya. Bai kamata a dubi kimar
mutum ko rashin kaurinsa, matukar ba ta/ya
furta munanan kalamai a lokacin da ya/take
bakin aiki, kuma ya/ta san yadda za a tarairayi
bakin da ake gudanar shirin da su,” kamar yadda
Beibers ta bayyana wa jaridar Gulf News.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "An dakatar da mata masu shirin talabijin a Masar saboda teva"

Post a Comment