Mutane 9 ne suka mutu a harin Maiduguri

A Najeriya, mutane tara ne aka tabbatar da sun
mutu lokacin da wasu da ake zargi 'yan kungiyar
Boko Haram ne suka kaddamar da harin bama-
bamai a Maiduguri, babban birnin jihar Borno.
Rahotanni sun ce wasu 'yan kunar bakin wake ne
suka tayar da bama bamai guda biyu, daya a
kusa da kofar shiga sansanin 'yan gudun hijira na
Bakassi, sannan dayan a wani gidan man NNPC.
Hukumar bayar da agajin gaggawa a kasar,
NEMA, ta ce wasu mutane 24 sun samu raunuka.
Birnin na Maiduguri dai ya sha fama da hare-
haren 'yan kungiyar ta Boko Haram, kodayake
yanzu ba safai ake kai masa hare-hare ba.
Dakarun sojin Najeriya na cewa suna bakin
kokarinsu na kawar da kungiyar ta Boko Haram,
suna masu kira ga mutane cewa su rika kai
rahoton duk wani motsi da ba su amince da shi
ba.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Mutane 9 ne suka mutu a harin Maiduguri"

Post a Comment