Sojoji sun dakile yunkurin sabon hari a Maiduguri

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta sun
dakile wani yunkuri na kai harin kunar bakin
wake a sansanin 'yan gudun hijira na Bakassi
dake Maiduguri, babban birnin jihar Borno.
An yi yunkurin kai harin ne kwana daya, bayan
wasu 'yan kunar bakin wake da ake zargi 'yan
kungiyar Boko Haram ne sun kai hare-hare a
birnin, ciki har da kofar shiga sansanin na
Bakassi.
Cikin wata sanarwa, kakakin rundunar sojin kasa
ta Najeriyar, Kanar Sani Usman Kukasheka ya ce
dakarun rundunar Operation Lafiya Dole dake
Maiduguri sun harbe wani dan kunar bakin wake
da safiyar Lahadi, yayin da yake kokarin kutsawa
cikin sansanin 'yan gudun hijiran na Bakassi.
Kanar Kukasheka ya ce bayan an harbe dan
kunar bakin waken, jami'ai tsaro masu kwance
bom sun lalata bom din dake jikinsa kafin ya kai
ga tashi.
Hare-haren kunar bakin wake na neman dawowa
a birnin na Maiduguri, bayan an samu saukin
hare-haren na lokaci mai tsawo.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Sojoji sun dakile yunkurin sabon hari a Maiduguri"

Post a Comment