Ubangiji kawai ke yi abinda yake so

– Wannan mutumin ya fadi cewa yaji murnar
Ubangiji yayin da yake addu’a
– Yace ance yaje yayi fada da zaki da
hannun sa, abunda ya faru ya zama abun
tausayi.
Yadda da Ubangiji da jin muryar shi babbar
baiwa ce, sai dai mutane da yawa sun kasa
banbanta muryar Ubangiji ta ainahi da
muryar shaidanun aljannu. Zasu ce sunji
muryar Ubangiji alhalin kawai zuciyar su ta
raya masu ko kuma yaudara ce irin ta
shaidanun aljannu.
Wani mutum dan kasar Buenos yace ya
samu umurnin da lahira , wai yaji muryar
ubangiji inda yace yaje yayi fada da zaki da
hannun sa, amma ya manta da wani abu mai
mahimmanci cewa duk wani abu na wahayi
ko mu’ujiza dole yayi dai dai da karantarwa
da littafi mai tsarki, in ka ki wannan gaskiyar
to hakika zaka fada cikin yaudara.

Ba wata aya a cikin littafi mai tsarki da tace
muyi fada da dabbobi masu hadari.
Mutumin ya saurari muryar ba dai dai ba,
kuma abun ya koma sai abun ya zamar mai
abun kaico, mutumin ya shiga gidan da ake
aje dabbobi sai ya haura katanga ya shiga
gurin da ake boye zakuna,ya fara fada da
zaki, har zakin ta kashe shi.
Wannan ya nuna cewa ba muryar ubangiji
yaji ba, saboda ubangiji ba ze taba tura ka
inda za’a kashe ka ba, kuma ubangiji ba ze
taba cewa kayi fada da wani ba.
Kullum kari ka sauraren abu da kyau karka bi
hudubar shaidan.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Ubangiji kawai ke yi abinda yake so"

Post a Comment