Nigeria: An maido da abincin 'yan gudun hijira da aka sace

Jami'ai a jihar Borno ta Nigeria sun ce an
hannunta musu abincin da gwamnatin tarayyar
kasar ta aike wa 'yan gudun hijirar rikicin Boko
Haram da shi amma sai aka karkata akalar wasu
daga cikin motocin da ke dauke da kayan
abincin.
Shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta
jihar Alhaji Ahmed Satomi ya tabbatar wa BBC
da cewa sun karbi motoci 79 na kayan abinci
daga cikin 113 da gwamnatin tarayyar ta turo;
kuma nan ba da dadewa ba za su karbi sauran.
'' Ministan da aka wakilta ya kawo kayan abincin
ne ya zo ya kawo wannan abincin da ake tunanin
an so a bi wata hanya da shi, amma
alhamdulillahi yanzu an gano shi har an
hannunta shi ga gwamnatin jihar Borno.'' In ji
Alhaji Satomi.
Zargin karkata akalar kayan abincin na 'yan
gudun hijra dai ya fusata mutane da dama a
kasar tun ma ba 'yan gudun hijiran ba wadanda
suka yi zanga-zanga a sansanoni daban-daban

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Nigeria: An maido da abincin 'yan gudun hijira da aka sace"

Post a Comment