Sojojin Najeriya sun harbe wani dan kunar bakin wake

Rahotanni daga garin Maiduguri sun nuna
cewa dakarun sojojin Nijeriya sun bindige
wani dan kunar bakin wake dake dauke da
bama-bamai har guda biyu a jikin sa,
 a
lokacin da ya yi yunkurin shiga sansanin
‘yan gudun hijira na Bakassi dake garin
Maiduguri a safiyar yau.
Idan ba a manta ba, a sanyin safiyar jiya
Asabar ma an samu tashin tagwayen bama-
bamai a wannan yankin, inda kimanin
mutane tara suka rasa ransu yayin da
mutane da dama suka ji rauni.
A wani labarin mai kama da wannan kuma a
jiya ne dai A Najeriya, mutane tara ne aka
tabbatar da sun mutu lokacin da wasu da
ake zargi ‘yan kungiyar Boko Haram ne suka
kaddamar da harin bama-bamai a Maiduguri,
babban birnin jihar Borno.
Rahotanni sun ce wasu ‘yan kunar bakin
wake ne suka tayar da bama bamai guda
biyu, daya a kusa da kofar shiga sansanin
‘yan gudun hijira na Bakassi, sannan dayan a
wani gidan man NNPC.
Hukumar bayar da agajin gaggawa a kasar,
NEMA, ta ce wasu mutane 24 sun samu
raunuka.
Birnin na Maiduguri dai ya sha fama da hare-
haren ‘yan kungiyar ta Boko Haram,
kodayake yanzu ba safai ake kai masa hare-
hare ba.
Dakarun sojin Najeriya na cewa suna bakin
kokarinsu na kawar da kungiyar ta Boko
Haram, suna masu kira ga mutane cewa su
rika kai rahoton duk wani motsi da ba su
amince da shi ba.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Sojojin Najeriya sun harbe wani dan kunar bakin wake"

Post a Comment