Kwararrun masana a Saudiyya sun kafa kungiyar auren zawarawa

Wasu kwararrun masana a kasar Saudiyya da
suka hada da likitoci da Injiniyoyi da malaman
addini da Farfesoshin jami’a, sun kafa kungiyar
auren zawarawa da matan da mazansu suka
mutu, ta hanyar bin ka’idar auren mace fiye da
daya a dokar shari’ar Musulunci da ta amince a
auri hudu.
Kafafen yada labaran Saudiya sun ruwaito cewa,
akwai matan da ba su da aure da suka kai
miliyan biyu, wadanda suka hada da matan da
mazajensu suka mutu da wadanda aka sake su
da ma wadandfa ba su taba yin aure ba. A
karkashin dokar Saudiyya irin wadannan matan
an yarda su sake yin aure, amma ba a cika
aiwatar da dokar ba.
“Za mu yada manufar auren mace fiye da guda,
kuma ya kamata mata su amince da ita, don
bayar da dama ga wadanda ba su da aure su
samu mazan aure,” a cewar jigon da ya kafa
kungiyar, Ataallah Al Abar.
Abar ya ce ya mika wa hukumomi takardun
bayanai da ke nuni da tsarin kafa kungiyar.
Sannan kungiyar za ta samar da shafin
sadarwarta, wanda za baje tsarin auratayya
tsakanin maza da mata.
Auren mace fiye da daya, al’amari ne da aka
saba da shi tunda addini ya amince a auri mata
hudu a lokaci guda.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Kwararrun masana a Saudiyya sun kafa kungiyar auren zawarawa"

Post a Comment