Nigeria: Satar Mutane ta yi kamarin da ba a zato

Wani dan majalisar wakilan Najeriya ya ce
matsalar satar mutane domin karbar kudin fansa
a wasu jihohin kasar ta yi kamari fiye da yadda
kowa ke tsammani.
Hon. Abdulmalik Zubairu daga jihar Zamfara -
daya daga cikin jihohin da ke fama da wannan
matsalar- ya ce a mazabar da yake wakilta kadai
an sace mutane kusan bakwai a cikin makonni
biyu kawai.
Ya ce yanzu masu garkuwa da mutanen kan bi
mutane har gidaje ko gonakkinsu su sace su.
Shi ma da yake zantawa da BBC bayan yin gyara
da dokar hukunta masu satar mutane domin ta
hada da hukuncin kisa, Kakakin Majalisar
Dokokin jihar Kano Honourable Kabiru Alhassan
ya ce ko a kudancin jihar ma ana bin mutane har
gona ana garkuwa da su.
Wakilin BBC a jihar ta Kano ya ce wannan
matsalar na sa har mazauna wannan yankin na
kauracewa gidajensu.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Nigeria: Satar Mutane ta yi kamarin da ba a zato"

Post a Comment