Kyawawan halayen Hadiza Gabon

Hadiza ko kuma Dijatou Aliyu wadda aka fi
sani da Hadiza Gabon, tana daya daga cikin
jarumai mata da suka shahara a farfajiyar
finafinan Hausa. Hadiza ta yi matukar
kwarewa a duk wani matsayin da za a ba ta
a fim, wanda hakan ya sa har yau ake
damawa da ita a masana’antar, domin ba
kowace jaruma ba ce za ta iya hawa irin
matsayin da jarumar ke hawa a finafinai.
Fitacciyyar Jarumar Kannyywood, Hadiza
Gabon
Kyakkyawar jarumar ta kuma kasance mai
yawan masoya daga cikin jaruman fim, har
ta kai ga ta samu daukakar da ita kanta ba
ta taba zaton samu ba.
Allah ya azurta jarumar da kyawawan dabi’u
na taimako, tausayi da jin kan mutane,
musamman gajiyayyu, marasa karfi da kuma
marayu.
Akwai lokacin da labarin wata nakasashiyar
yarinya mai suna Rahama Karuna wacce ake
dauka a cikin roba ana bara da ita a jihar
Kano, lokacin da Hadiza ta ji labarin wannan
yarinya sai ta tausaya sosai harma ta ziyarci
yarinyar inda ta tallafa mata da kudade da
kayayyakin abinci.
Sannan kwanakin baya Hadiza ta ziyarci
sansanin yan gudun hijira inda su ma tayi
masu alkhairi mara misali, domin ta tallafa
masu da kayan abinci, kamar yadda muka
sani cewa yan gudun hijira sunyi fama da
lalurar yunwa.
Hadiza Gabon a lokacin da ta kai ziyara
sansanin yan gudun hijira
Bayan nan kuma a lokacin da jaruma Hadiza
za ta yi bikin zagayowar ranar haihuwarta,
maimakon ta tara jama’ar da ba su dace ba
a yi ta sharholiya, sai ta tattara kayayyakin
bikin nata ta je gidan marayu, inda ta dauke
su a matsayin wadanda za su taya ta bikin.
Hadiza ta yanka kek din bikin ranar
haihuwarta ta tare da marayun kuma ta ci ta
sha tare da marayun, domin a cewarta yin
hakan wata hanya ce ta farantawa marayun
rai, tare kuma da debe musu kewa, wanda
bai kamata a ce ana mayar da su saniyar
ware ba a al’amuran farin ciki dake gudana a
kasar nan.

Hadiza Gabon tare da wasu yara
Wannan ba shi ne karo na farko da Hadiza ta
kai ziyara gidan marayu ba, domin aikinta ne
ziyara gidan marayun inda take raba musu
kayan abinci da kayan sawa.
Munayi wa wannan jaruma fatan alkhairi da
kuma ci gaba a rayuwarta ta duniya da
lahira.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "Kyawawan halayen Hadiza Gabon"

Post a Comment