Fatma Samoura za ta kai ziyara Saliyo

Sakatariyar Hukumar Kwallon Kafa ta Duniya,
Fifa, Fatma Samoura, za ta ziyarci Saliyo domin
sasanta rikici tsakanin hukumar kwallon kafar
kasar da shuwagabannin siyasar kasar.
Fifa ta bukaci yin taro tsakaninta da Shugaban
kasar Saliyo, Ernest Bai Koroma, da kuma
jami'an hukumar kwallon kafar kasar.
Haka kuma Samoura na son tattaunawa kan
batun cogen wasa da ya shafi Saliyo a shekarar
2008.
A shekarar 2014 aka dakatar da 'yan wasa 15 da
wasu jami'an Saliyo kan zargin cogen wasan da
suka yi da Afirka ta Kudu a wasan shiga gasar
cin kofin duniya.
Tun a farkon ba ne hukumar kwallon kafa ta
Saliyo ta kafa kwamitin bincike ta kuma mikawa
shuwagabannin kasar abin da ta gano, amma har
yanzu ba a dauki mataki ba.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

Related Posts :

  • Na fi so Ronaldo ya lashe Ballon d'Or — Zidane Kocin Real Madrid Zinedine Zidane ya ce Cristiano Ronaldo ne ya fi cancanta ya zama zakaran kwallom kafar duniya duk da cewa bai zu… ...
  • FA tana tuhumar David Moyes Hukumar kwallon kafar Ingila tana tuhumar kocin Sunderland David Moyes da zargin aikata ba daidai ba bayan an kore shi daga filin wasa rana… ...
  • Kompany zai ci gaba da murza leda a City -Guardiola Kocin Manchester City Pep Guardiola ya ce Vincent Kompany na da kyakkyawar makoma a kungiyar, amma yana bukatar sadaukawar domin ya rika … ...
  • A ranar Asabar za a ci gaba da buga gasar La Liga wasannin mako na 10. Sai dai Cristiano Ronaldo na fama da rashin cin kwallaye a gasar ban… ...
  • Ba za mu kori Rooney ba —Mourinho Kocin Manchester United Jose Mourinho ya ce babu inda kyaftin din kungiyar Wayne Rooney zai je. Mourinho ya yi watsi da rahotannin da ke … ...

0 Response to "Fatma Samoura za ta kai ziyara Saliyo"

Post a Comment