'Jacob Zuma ya tsallake rijiya da baya'

Shugaban kasar Afrika ta kudu Jacob Zuma ya
tsallake kuri'ar yanke kauna da 'yan Majalisar
dokoki suka kada a kansa.
Babbar jami'yyar adawa ta Democratic Alliance
ita ce ta gabatar da kudurin kan abin da ta kira
sakacin da yake yi a shugabancin kasar.
Jamiyya mai mulki ta ANC da ke da rinjaye a
Majalisar ta goyi bayan shugaba Zuma.
Wakiliyar BBC ta ce wannan shi ne karo na uku a
wannan shekarar da aka kada kuri'ar yanke
kauna akan shugaba Zuma kuma jamiyyar ANC
mai mulki dake da rinjaye a majalisar dokoki ta
shawo kansu ba tare da wata matsala ba.

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

0 Response to "'Jacob Zuma ya tsallake rijiya da baya'"

Post a Comment